Thursday, August 23, 2007

Maryam Hiyana & Suleiman Bobo

Assalamu Alaikum!
Hakika Suleiman (Bobo) da Maryam Hiyana sunyi kurkure ba karami ba, koda ma a wanne addini ne. Amma mu sauran musulman duniya abin da yakamata da mu shine; Kamar yadda yake a musulunce yadda d akaddara rabin imani ne. Wannan abu Allah ya riga da ya kaddara sai fara babu wani dan Adam ko Aljani da ya isa ya kawar da shi, dole sai ya faru. Hakika sunyi kuskure matuka ("Allah ya gafarta musu"). Jama'a ina so ku sani fa, babu wani wadda ya fi karfi wanna abu ya faru shi. Amma tunda sunyi nadama, shikenan in har sauran musulmai na duniya da hakki a kan wannan abu da ya faru. Dan Allah a gafarta musu kamar yadda Shi Suleiman din ya bukaci Musulman duniya da su yafe masa. Kuma ku sani cewa, Allah ubangiji yana yafewa wadda ya yafewa dan uwansa. Saboda yada wannan hoto na bidiyon Hiyana ba zai haifar maka da komai ba Illa raga darajar musulunci da al'adar Hausawa a idon duniya.

1 comment:

alkalami alkalami alkalami said...

HAUSA FIM: TARBIYAR TSIRARA

HAUSA FIM: TARBIYAR TSIRARA
AUWAL MUHAMMAD ABDULKADIR
aazarema@yahoo.com
6/8/1428h-19/8/07m

BISMILLAHIRRAHMANIRRAHIM
Sanannen abune cewa kasashe masu kaffa-kaffa da
addinin su da al'adunsu na kwarai suna kokarin maida
finafinai da wasan kwaikwayo wata kafa ta tattauna matsalar
alumma da tarbiya da bada tunani na gari, sabanin halinda
muke a kasar hausa na karkatar da wannan dama zuwa
gwada kwarewa wajen nuna rashin kunya da da koyawa
manyan gobe munanan dabi'u daga baya kuma sai ace ana
kokarin gyara tarbiya to lallai bamu ba tarbiya har duniya ta
tashi indai yan daba da mata masu cin gashin kansu da
wadanda aka kasa tarbiyarsu suka gudu suka bar tarbiya su
-ne masu tarbiya kai abun dariya da takaici duk da haka
shuwagabanni da wadanda abun ya shafa basu yi yunkurin
hanawa ko kokarin garkatar da akalar fina-finan izuwa koyar
da tarbiyar gaskiya ba . to yanzu abun yakai ga dole kowa ya
ciza yatsa , akwai matukar da takaici ace yar fim ta fito tsirara
har na tsawon dakikai takwas kan gado sannan wani yazo ya
haukanta yayi tsiyar da zaiyi da ita, sannan yayi wani irin
nau'i na wasa da maniyinsa kan cinyarta , kai ! wallahi ,
na'uzu billahi minashshaidanirrajim! wani irin dabbanci kenan?
kuma abun mamaki harda cewa '' a gafarcemu'' amma
wannan yarinya taci sunanta ''HIYANA'' don kuwa ta ha'inci
duk musulmin duniya, ta kuma tona asirin musulmin najeriya.
Duk wani mai zurfin tunani yasan hakan zata faru tunda
kokari suke su kwaikwayi [nigerian film] su kuwa wannan ba
bako bane gunsu, ga wani abunda na taba karantawa jaridar
gaskiya tafi kwabo ''GTK: To, a matsayinki na wadda take fitowa a fina-finan
Hausa da na Turanci, yaya za ki kwatanta bambancin da ke
tsakanin fina-finanmu na Arewa da kuma na Kudanci?
HAUWA MAINA: Ai dai wannan ne ko kuma aka tambaya, za
ku iya fadin bambancin (dariya).
GTK: Amma da yake ke kina cikin harkar ne, ina ganin ke ya
fi cancanta ki yi mana bayani.
HAUWA MAINA: To shi kenan, a gaskiya, ’yan Kudu sun yi
mana fintinkau in dai za a yi maganar gaskiya ce. Amma
Alhamdulillahi mu ma mun fara shiga sahunsu, saboda idan
aka yi la’akari da irin na’urorin da suke amfani da su, to,
yanzu mu ma mun fara samun irin wa]dannan na’urorin. Haka
kuma ’yan wasanmu na Hausa su ma yanzu sun zaburo, suna
kuma kokari sosai. Saboda haka nan ba da jimawa ba za mu
rika hada kafada da kafada da su.''

Hakika abun daya ban mamaki cikin wannan al'amari babu
kamar wasu masu kokarin wanketa da cewa ai ba fim din
tsiraici bane, saboda wannan wani abu ne tsakaninta da
saurayinta bai da alaka da fim, to amma ai ita jaruma ce a
wannan harka ta tarbiya, wa ya sani ko ta sadaukar da kanta
ne wajen gyara al'adun banza har ta fara yada tarbiya kyauta
ana yada ta a blue tooth cikin kayan mutunci , domin ayi koyi
da ita, sannan an sakar muku haka ne , shin wannan baya
gwada cewa wata ran za'a yi hakan a tsare da furodusa da
dukkan shikashikai da sharuddan fim.

sannan wasu kuma sun bige da cewa taci mutuncin hausa-
fulani ina ruwan wannan matsala da hausa fulani , wasu na
cewa daman ba hausawa bane masu yi , hakika wannan
karya ce mai girma da neman wanke kai na banza da wofi ,
to kai in ma haka ne , waya basu izinin shigowa kano, jama'a
kar mu rudi kammu, hausa fulani dai a duniya zamu bar shi
ba wani abu mai anfani gun Allah sai musulunci.

IYAYE : sune kashin bayan tarbiyar 'ya'ya kuma sune
matakin da idan yaro ya rasa ko sukai sakaci dashi rayuwarsa
zata shiga wani yanayi wanda bara aji dadin karshenta ba,
wani yana cewa '' uwa makaranta ce idan ka shirya ta kamar
ka shirya al'umma ne'' kuma kamar yadda kowa ya sani
wadannan masu cin abinci da lalata tarbiyar manyan gobe
galibinsu in bamu ce duka ba sun fuskanci matsala da iyaye
kamar auren dole ko rashin mai riko mai kyau ko rashin tsawa
da kwaba don haka dole iyaye su dau hakurin daukan kaso
mai girma na laifi saboda kaso mai girman ba suke dashi
wajen jibintan yayansu da kuma damar tarbiya.

YAN WASA: saboda sune masu fuskantar da wannan
matsala zuwa ga alumma kai tsaye don haka duk da barrantar
da kan- su da wasu uzurori da suke bayarwa wanda zai yi
wuya su kansu su yarda da su a cikin zukatansu balle
al'umma gaba daya. Su dai kokarin su dole sai sun kwaikwayi turawa alhali kuwa
kowa yana kokarin bada gudumawane daidai al'ummarsa,
idan bature da baturiya sukai wani rashin kunya a wasan
kwaikwayo to saiku duba cewa to shin kowa a cikin jama'arku
ba rike ya ke da addini ba ? ba tare yake da mafadi ba? Shin
burgewa a garemu shine mu fita daga shingen iyaye da
sunan yanci? Wadannan banbance-banbance na addini da
al'ada idan ba'a duba su ba to zamu jima cikin wannan rami,
mu fito mun yi kura duk wanda ya kallemu ba zai iya
maimaitawa ba.

SHUGABANNI: wato duk Wanda yake da damar fada aji
amma bai hango matsalar da zata iya jawowa masu
zuwa ba, ko ya hango baiyi kokarin kawo sauyi ba .

Daga karshe ina kara rokon wanda abun ya shafa da suyi
hattara wajen daidaita wannan wasa inda zaiyi daidai da
addinin jama'arsu da al'adunsu na kwarai , inba haka ba muyi batan bakatantan bamu ga namu bamu ga nasu .

Allah ya raba mu da sharrin shaidan.